UNICEF ta ce an kashe 'yan makaranta a Syria
Hukumar UNICEF ta ce yaran makaranta 22 ne aka kashe tare da malaman su 6 lokacin da hare haren sama da ake kai wa Syria ya fada kan wata makarantar da ke Yankin Idlib.
Wallafawa ranar:
Daraktan UNICEF Anthony Lake ya bayyana wanann kazamin harin da aka kai kan makarantar yara a matsayin abin takaici, inda yake cewa babu abinda ya raba shi da laifufukan yaki.
Lake ya ce da gangan aka kai harin, ganin cewar ba sau daya aka kai shi ba.
Kungiyar da ke sa ido kan rikicin Syria ta ce jiragen yakin da suka kai hari kan wannan makaranta kuma suka kashe daliban sun fito ne daga kasar Rasha ko kuma Syria.
Jakadan Rasha a Majalisar Dinkin Duniya Vitaly Churkin ya yi Allah wadai da harin.
Samantha Power, Jakadiyar Amurka ta soki Rasha wadda ta ce taki hada kai da Majlisar Dinkin Duniya dan warware rikicin Syria, yayin da Kwamishinan Jinkai Stephane O’Brien ya bukaci daukan mataki.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu