Isa ga babban shafi
Syria

Zafafa hari kan Aleppo ya raba mutane miliyan 2 da samun ruwa

Zafafa kai hari kan birnin Aleppo da sojojin Syria ke yi ya raba kimanin mutane miliyan biyu da samun ruwa.

Wani sashin birnin Aleppo da harin jiragen yaki ya rusa
Wani sashin birnin Aleppo da harin jiragen yaki ya rusa Reuters
Talla

Majalisar Dinkin Duniya ta ce sabbin hare-haren da aka kaddamar ya lalata ilahirin tashar da ke tura ruwa zuwa abashin birnin na Aleppo da ke karkashin ikon ‘yan tawaye.

Jami’an Majalisar Dinkin Duniya sun ce domin kare tashar ruwan da ta yi saura daga lalacewa, dole aka rufe ta, kasancewar ita ke bawa sauran sassan birnin na Aleppo ruwa.

Wani mai magana da yawun sashin kula da yara na majalisar Dinkin Duniya Kieran Dwyer, ya ce rashin ruwan wata sabuwar barazana ce ga mazauna Aleppo, kasancewar shan ruwa marar tsafta zai haifar da barkewar cututtuka.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.