Isa ga babban shafi
Syria

Turkiya ta kai hari kan mayakan Kurdawa

Rundunar mayakan Kurdawa da ‘yan tawayen Syria, ta ce jiragen yakin Turkiya sun yi luguden wuta kan muhimman wuraren da ke karkashinta dab da birnin Jarabulus da ta karbe daga mayakan IS.

Motocin sulke na sojin Turkiya yayin tunkara iyakar kasar da Syria
Motocin sulke na sojin Turkiya yayin tunkara iyakar kasar da Syria REUTERS/Umit Bektas
Talla

Mayakan sun kara da cewa harin jiragen Turkiyan ya yi sanadiyyar mutuwar fararen hula da dama, lamarin da ta bayyana a matsayin tsokana.

Cikin satinnan ne dai rundunar sojin Turkiya da kaddamar da hare hare kan mayakan ISIL da na Kurdawa da ke cikin Syria.

Shugaban Turkiya Recep Tayyib Erdogan ya ce kaddamar da hari kan 'yan ISIL da ke Syria ya zama dole don kare kasar daga hare-haren ta'addanci da ke karuwa a kasar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.