Syria
'Yan tawayen Syria sun harba roka a Damascus
'Yan tawayen Syria sun harba makamin roka tsakiyar birnin Damascus bayan wani kazamin harin da sojojin gwamnati suka kai asibitin garin Aleppo.
Wallafawa ranar:
Talla
Kungiyar da ke sa ido kan rikicin Syria ta ce mutane 8 suka mutu a harin na Damascus yayin da wasu 20 suka samu raunuka.
Rahotanni sun ce an kai harin na Aleppo ne a asibtin Al Shaar inda aka kashe wani jariri mai kwanaki biyu.
Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana Syria a matsayin kasa mafi hadari ga jami’an kiwon lafiya, inda kididdiga ta nuna hare-hare 135 kan asibitoci a kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu