Isa ga babban shafi
Afghanistan

Adadin mamata ya karu a Afghanistan

Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewar adadin mutanen da suka mutu a kasar Afghanistan a cikin watanni shida da suka gabata ya karu saboda yadda masu kai wa kasar hare-hare  suka dada kaimi.

'Yan ta'adda sun kara kaimi wajen kai hare-hare a Afghanistan, abinda ya haddasa karuwar mamata a kasar
'Yan ta'adda sun kara kaimi wajen kai hare-hare a Afghanistan, abinda ya haddasa karuwar mamata a kasar REUTERS/Omar Sobhani
Talla

Rahotan wanda ofishin majalisar da ke birnin Kabul ya fitar, ya nuna cewar tsakanin watan Janairu da Yuni na bana, an kashe fararen hula dubu 1 da 601 yayin da dubu 3 da 565 suka  samu raunuka.

Wannan ya nuna cewar an samu karuwar kashi 4 cikin 100 na adadin mamatan da aka samu a shekarar 2015.

A jiya lahadi ne, al'ummar kasar suka yi zaman makoki don juyayin kazamin harin da kungiyar IS ta kaddamar kan masu zanga-zangar lumana a birnin Kabul, inda ta kashe mutane 84.

Shugaban kasar Asraf Ghani ya sha alwashin daukar fansa kan wadanda suka kitsa harin wanda aka bayyana a matsayin mafi muni da kasar ta Afghanistan ta gamu da shi a cikin shekaru 15.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.