An soma taron kawo karshen rikicin Syria
Yan adawar kasar Syria sun samu isowa birnin Geneva ,inda za su tattaunawa da wakilan MDD dama bangaren Gwamnatin kasar ta Syria tareda tattance hanyoyin da suka dace na gani an kawo karshen rikicin da ya mamaye kasar tsawon shekaru biyar.
Wallafawa ranar:
Sai da rahotani daga birni Geneva na nuni cewa yanzu hakka yan Adawa na ikirarin cewa za su janyewa daga wannan tattaunawa har in dakarun Gwamnatin shugaba Bashar Assad suka ci gaba da kisan fararen hula.
Kokarin MDD na hada kungiyoyin da basa ga maciji da juna na ci gaba da fuskantar jan kaffa duk da yake ana sa ran gani za su cimma matsaya ta gari.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu