ISIS ta hallaka fararen hula da sojoji a Syria
Wani hari da kungiyar ISIS mai da’awar jihadi ta kai a birnin Deir Ezzor da ke gabashin Syria ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 85 da kuma sojojin gwamnati 50 kamar yadda kungiyar da ke sa ido kan hakkin adam a Syria ta sanar.
Wallafawa ranar:
Shi kuwa kamfanin dillancin labaran Syria da ake kira SANA ya rawaito daga mazauna yankin cewa, kimamin fararan hula 300 ne suka rasu sakamakon farmakin na jiya Asabar.
Matukar dai aka tabbatar da haka, to lalllai zai kasance daya daga cikin manyan munanan hare haren da suka hallaka jama’a da dama a rana guda a cikin kusan shekaru biyar da aka kwashe ana fama da yaki a kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu