Mata sun shiga zaben Saudiya a karon farko
An fara jefa kuri’a a zaben farko a tarihin kasar Saudiya da ya kunshi Mata ‘Yan takara da masu jefa kuri’a a yau Assabar.
Wallafawa ranar:
Wannan ne karo na farko da Mata zasu kada kuri’a, sannan sama da 900 suka tsaya takara a zaben kananan hukumomi.
Maza kimanin 6,000 ke takara a zaben da kunshi yawan kujerun shugabanni 284.
Sai dai ana ganin yana da wahala matan su lashe zaben saboda dokokin Saudiya na haramta cudanya tsakanin maza da mata a waje guda.
Har yanzu dai a Saudiya an haramtawa Mata tukin Mota, sannan ba su iya fita balaguro sai da izini tare da rakiyar muharraminsu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu