Isa ga babban shafi
Syria

An kashe dan Jaridar Anatolia a Syria

Wani dan jarida mai daukar hoto dake yi wa kamfanin dillancin labaran Anatolia na kasar Turkiya aiki a kasar Syria, ya rasa ransa a cikin wani harin kunar bakin wake da aka kai a yankin Aleppo dake arewacin kasar ta Syria.

Yankin Aleppo na Syria na fama da hare hare
Yankin Aleppo na Syria na fama da hare hare REUTERS/Jalal Al-Mamo
Talla

Saleh Mahmoud Laila mai shekaru 27 ya rasa ransa ne tare da wasu mutane akalla 19 a harin wanda aka kai a kasuwar garin Hraytan dake yankin Aleppo, inda ake tafka kazamin fada tsakanin mayakan Jihadi na ISIS da ‘yan tawaye masu adawa da su.

A watan yulin da ya gabata ne Laila ya tsira daga hare haren jiragen sama da dakarun shugaba Bashar al-Assad su ka kaddamar, yayin da ya yi fama da jinya sakamakon raunukan da ya samu a hare haren, inda aka kwantar da shi a wani asibiti da ke Turkiya.

Tuni dai shugaban kasar Turkiya Recep Tayyip Erdogan ya bayyana bacin ransa kan mutuwar dan jaridar tare da mika sakon ta’aziya ga iyalansa da kuma kamfanin dillacin labaran na Anatolia.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.