Mutane 27 sun mutu a hatsarin jiragen kasa biyu a india
Hukumomin Kasar India sun tabbatar da mutuwar mutane kimanin 27 yayin da wasu da dama suka jikkata sakamakon kauce hanya da wasu jiragen kasa biyu suka yi lokacin da suke kokarin tsallaka wata gada da ambaliyar ruwa ya lalata a Jihar Madhya Pradesh.
Wallafawa ranar:
‘Yan Sanda sun ce an yi nasarar ceto daruruwan fasinjojin da hatsarin ya rutsa da su amma wasunsu da dama suka samu raunuka.
Jiragen kasa na daga cikin hanyar sufuri mafi sauki a kasar India.
Lamarin dai ya faru ne a kusa da garin Harda a cikin dare kusan karfe 12.
Yanzu haka gwamnatin Firaminista Nerendra Modi ta bukaci gudanar da binciken musabbabin faruwar hatsarin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu