Sabon shugaban Taliban na Fuskantar soka
Sabon shugaban kungiyar Taliban Mullah Akhtar Mansour ya yi kiran neman hadin kan ‘ya’yan kungiyar bayan shan soka daga wani bangare na kungiyar da ke ganin babu adalci a zabensa.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Mullah Akhtar Mansour ya yi wannan kiran ne a wani sakon muryar da ya aike karon farko, da sanar da shi a matsayin sabon Jagoran kungiyar bayan tabbatar da mutuwar Mullah Omar.
Sa’o’i kadan bayan nada sabon shugaban tun a jiya Juma’a, wasu bangarorin kungiyar suka fara sokar nadin, a wani al’amarin da suka bayyana shi a masatyin son kai wajen zabo sabon Jagoranasu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu