Isa ga babban shafi
Cambodia

Ana kama dan kasuwan kasar Cambodia da ya ci zarafin wata mace

Yau Asabar ‘yan sandan kasar Cambodia suka kama wani hamshakin dan kasuwa da ake nema ruwa a jallo, bayan da aka aka nuna shi cikin wani hoton Bidiyo yana dukan wata mace mai gabatar da shirin gidan Talibijin.

Fraiministan kasar Cambodia, Hun Sen
Fraiministan kasar Cambodia, Hun Sen @rfi/siv channa
Talla

Tun lokacin da hoton ya bayyana, jama’a suka yi ta bayyana bacin ransu a kai, lamarin da ya sa Jami’an tsaro ke neman dan kasuwan mai suna Sok Bun, ruwa a jallo.
Bayan fara neman sa ne Sok ya tsere zuwa kasar Singapore, sai dai a loacin da ya dawo kara yau Asabar jami’an tsaro suka cafke shi a filin jirgin samana Phnom Penhm inda aka tasa keyar sa.
Hotunan Bidiyon sun nuna dan kasuwan mai shekaru 37 a duniya, dake harkar gine gine, yana dukan Ek Socheata, da aka fi sani da sunan SaSa, a wani wajen cin abinci.
Masu gabatar da kara sun ce mutumin ya amsa laifin, kuma yanzu haka ana tsare da shi a wani gidan yarin dae Prey Sar, inda zai iya fuskantar hukuncin daurin shekaru 5 kan laifin.
Dama ana gani kasar ta Cambodia a matsayin inda inda masu hannu da shuni ke take doka ba tare da bangaren shari’a ya iya yin wani abu ba a kai, kuma cin zarafin mata abu ne da ya zama ruwan dare a kasar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.