Isa ga babban shafi
Malaysia

MH17 : Ana zaman makoki a Malaysia

Al’ummar kasar Malaysia suna zaman makoki bayan isowar gawarwakin mutane 20 cikin wadanda suka mutu a hadarin jirgin kasar MH17 da ya tarwatse a kasar Ukraine. Sarki Abdul Halim Mu’adzam Shah tare da Firaminista Najib Razak ne suka jagoranci jami’an gwamnati a filin jirgin saman birnin Kuala Lumpur, domin karbar gawarwakin.

Gawarwakin Fasinjan jirgin MH17 20 da suka iso Malayasia
Gawarwakin Fasinjan jirgin MH17 20 da suka iso Malayasia REUTERS/Olivia Harris
Talla

Jirgin kamfanin Jiragen saman kasar Malaysia mai lamba MH17 dauke da mutane 298, ya tarwatse ne a lardin gabacin kasar Ukraine, a wani yanayin da ake ganin harbo jirgin aka yi a kasar mai fama da rikici a ranar 17 ga watan Yulin da ya gabata.

An dakatar da bukukuwa a kasar Malaysia tare da sassauto da tutar kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.