An kwashe Sinawa sama da dubu uku daga Vietnam
Hukumomin kasar Vietnam sun baza dimbin jami’an tsaro domin bai wa ‘yan asalin China da ke zaune kasar kariya, bayan da al’ummar kasar suka kaddamar da boren nuna adawa da ‘yan kasar ta Sin.
Wallafawa ranar:
Yanzu haka dai ‘yan asalin China biyu ne suka rasa rayukansu tare da raunata wasu 135, lamarin da ya tilasata wa hukumomin birnin Beijing kwashe Sinawa sama da dubu uku daga kasar domin mayar da su gida.
‘Yan kasar ta Vitnam sun tayar da wannan bore ne bayan da ma’aikatan wani kamfanin hako mai na China suka fara aiki akan wasu tsibirai da kasar ta Vietnam ke ikirarin cewa mallakinta ne.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu