Malaysia: Jirgi MH370 ya yi hadari ne a tekun India
Firaministan kasar Malaysia Najib Razak ya bayar da sanarwar cewa Jirgin saman kasar da ya bata sama da makwani biyu da suka gabata dauke da fasinjoji 239, ya fadi ne a cikin tekun India, kuma yace dukkan mutanen da ke ciki jirgin sun rasa rayukansu.
Wallafawa ranar:
Firaministan yace sun tabbatar da haka ne daga gamsassun bayanai a tauraron dan Adam a yankin da jirgin ya fadi a teku.
Akwai sakon kar-ta-kwata da gwamnatin Malaysia ta aikawa ‘yan uwan mutanen da ke cikin jirgin da ya bata mai dauke da sakon cewa jirgin ya bata kuma babu fasinjan da ya rayu a cikinsa.
Kasashe da dama ne suka shiga aikin neman jirgin Malaysia a tekun India kusa da Australia bayan an hango wasu abubuwa masu kama da tarkacen jirgin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu