Isa ga babban shafi
Maldives

Kotun kolin Maldives ta haramta gudanar da zaben shugaban kasa

Kotun kolin kasar Maldives, a yau lahadi ta haramta gudanar da zaben shugabancin kasar zagaye na biyu, a daidai lokacin da hambararren shugaban Mohamed Nasheed ke kyautata zaton samun nasara domin sake dawowa a kan mukaminsa.

Akwatin kada kuri'a a Maldives
Akwatin kada kuri'a a Maldives REUTERS/Dinuka Liyanawatte
Talla

Wannan ne dai karo na uku da kotu ke haramta gudanar da zaben, lamarin da ke neman jefa wannan karamar kasa da ke tekun India a cikin wani mummunan rudani na siyasa.

A karshen makon da ya gabata hukumomin kasar sun tabbatar da cewa za a gudanar da zaben, lamarin da ya cutura bayan hukuncin kotun kolin.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.