Pakistan ta yi watsi zargin kisan Sojin India a Kashmir
Sojin kasar Pakistan sun musanta zargin kisan dakarun Sojin India guda biyar a wani hari da aka kai a yankin Kashmir. Kakakin Sojin kasar yace babu wani Sojansu da ya keta kan iyakar India. Gwamnatin India d tana zargin Pakistan ne da aikata kisan Sojojin a yankin Jammu da Kashmir inda ministan kasar yace an kai wa Sojojin ne harin kwantar bauna.
Wallafawa ranar:
Yankin Kashmir yanki ne da bangarorin biyu ke ikirarin mallakinsu ne wanda suke takaddama tsawon shekaru 60 da suka gabata.
Wannan harin kuma na zuwa ne a dai dai lokacin da kasashen biyu ke shirin komawa teburin tattaunawa, wanda shi ne karo na farko tun da aka samu sauyin gwamnati a kasar Pakistan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu