Isa ga babban shafi
India

Kotu ta dage sauraren Shari'ar Fyade a India

Kotu a kasar India ta dage sauraron shari’ar fyade da kuma kisan kai da ake wa wasu matasa biyar, Shari’ar da yanzu haka ke dauke hankalin kasashen duniya. A lokacin zaman kotun mai shari’a ya kori ‘yan jaridu da wasu tarin lauyoyin da suka cika kotun, inda aka saurari shari’ar cikin sirri da kuma kwararan matakan tsaro.

Masu Zanga zangar ganin an hukunta wadanda suka yi wa wata yarinya Fyade a India
Masu Zanga zangar ganin an hukunta wadanda suka yi wa wata yarinya Fyade a India REUTERS/Amit Dave/File
Talla

Priya Hingorani, mai gabatar da kara a kotun koli, kuma mai fafutukar kare yancin mata, tace suna fatar ganin an kamala shari’ar cikin lokaci, tsakanin watanni biyu zuwa uku.

Yanzu haka dai akwai shari’un fyade da aka kwashe tsawon shekaru tara ana yi, abinda ke ci gaba da harzuka wadanda aka ci zarafin su.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.