Isa ga babban shafi
Indiya

An rataye dan bindigar Mumbai a Indiya

Hukumomin kasar Indiya sun rataye Mohammed Ajmal Amir Kasab, daya daga cikin ‘Yan bindigar da suka kai hari a Mumbai a shekarar 2008, wanda ya yi sanadiyar hallaka mutane 166. A yau Laraba ne aka rataye Kasab a gidan yarin Yerwada a Pune da ke yankin yammacin Jahar Maharashtra bayan shugaba Pranab Mukherjee ya yi watsi da koken Dan bindigar na neman Afuwa.

Mohammed Ajmal Amir Kasab a lokacin da ya ke hannun 'Yan Sandan India
Mohammed Ajmal Amir Kasab a lokacin da ya ke hannun 'Yan Sandan India Reuters
Talla

Kasab ne kadai cikin ‘Yan bindigan da ya tsira da ransa, kuma kotu t ayi watsi da daukaka karar da ya yi a farkon watan nan, abinda ya sa aka kai shi gidan yarin Mumbai.

A shekarar 2010 ne aka yanke wa Kasab hukuncin Daurin rai da rai bayan kama shi da laifukan yaki da suka hada da kisa da ta’addanci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.