Isa ga babban shafi
Iraki

Al’ummar Iraqi suna zaman makoki bayan mutuwar mutane 111

Al’umomin Kasar Iraqi, sun shiga juyayin rasa dimbin rayukan jama’ar kasar da aka yi a jiya Litinin, sakamakon wasu jerin haren haren da ba a taba ganin irinsu ba, a cikin shekaru biyu da suka gabata, da suka hallaka mutane 111.

Wasu mazauna birnin Bagadaza sun taru a wajen da wani dan kunar bakin ya dala bom inda mabiya shi'a ke gudanar da buki
Wasu mazauna birnin Bagadaza sun taru a wajen da wani dan kunar bakin ya dala bom inda mabiya shi'a ke gudanar da buki REUTERS/Saad Shalash
Talla

Hukumomin kasar sun ce, mutane 235 suka samu raunuka, a hare haren 28, da aka kai birane 19, wanda ya janyo suka daga sassan duniya.

Wadannan ne hare hare mafi muni da aka kai a kasar Iraki a dai dai lokacin da al’ummar Musulmi ke gudanar da Azumin watan Ramadan.

Hare haren na zuwa ne kwana daya bayan kai wani harin Bom da ya yi sanadiyar mutuwar mutane 17.

Jami’an kiwon Lafiya sun ce akwai mutane 18 da suka mutu a birnin Taji inda kuma mutane 29 suka jikkata.

Da misalin karfe Biyar na safiyar Litinin kuma wasu ‘Yan Bindiga suka kaddamar da hari a sansanin Soji da ke Albu Slaib da ke Gabas da birnin Dhuluiyah, inda suka kashe dakarun Sojin Iraki Bakwai.

Akwai wasu Jerin hare haren bama bamai da aka kai a Birnin Bagadaza da kuma wasu Birane da ke makwabtaka da birnin.

Har yanzu dai babu wadanda suka fito suka yi ikirarin daukar nauyin kai hare haren amma a kwanan baya kungiyar al Qaeda ta yi gargadin karbe ikon kasar Iraki.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.