Isa ga babban shafi
Syria-MDD

MDD ta nuna damuwa halin da ake ciki a Syria

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Ban Ki Moon, ya bayyana halin da ake ciki a kasar Syria a matsayin abinda ba za’a amince da shi ba, inda ya bukaci wakilan kwamitun Sulhu su hada kansu akan matsalar.Kalaman Sakataren na zuwa ne a dai dai lokacin da kwamitin ke shirin gudanar da wani taro yau Talata, dan amincewa da wani sabon kudiri akan Syria, muddin taki aiwatar da shawarwarin Kofi Annan, wanda aka nada a matsayin manzon musamman na MDD da kungiyar kasashen Larabawa. 

Talla

Kasar Rasha ta bukaci Syria ta zagaita wuta, dan baiwa jami’an agaji kai kaya ga mabukata a cikin kasar, yayin da ta musanta cewar, bata da jirgin yaki a gabar ruwan Syria.

Ma’aikatar harkokin wajen Rasha, ta ce jirgin dake gabar ruwan Syria tankin mai ne, amma ba jirgin yaki ba.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.