Isa ga babban shafi

Francophonie na fargabar zaben Guinea

Kungiyar Kasashen dake amfani da harshen Faransanci ta duniya La Francophonie ta bayyana damuwa kan shirin zaben rabagardamar kasar Guniea mai zuwa, musamman sahihancin rajistar masu kada kuri’u.

Shugaban kasar Guinea Alpha Condé
Shugaban kasar Guinea Alpha Condé WU HONG / POOL / AFP
Talla

Gargadin kungiyar na zuwa ne kwanaki 6 kafin zaben da za’ayi a kasar wanda Yan adawa suka bayyana a matsayin yunkurin shugaba Alpha Conde na cigaba da zama a karagar mulki.

Kungiyar tayi zargin cewar akwai matsaloli sosai a rajistar masu kada kuri’un kasar mai dauke da kusan sunaye miliyan biyu da rabi na bogi, ganin cewar kashi 98 na masu rajistar basu da takardun shaidar da za’a tantance su, yayin da wasun su sun mutu, wasu kuma basu kai shekarun kada kuri’u ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.