Faransa za ta tura karin dakaru 600 zuwa yankin Sahel
Faransa ta bayyana shirin tura karin sojinta sama da 500 zuwa yankin Sahel, inda a yanzu haka dakarunta dubu 4 da 500 ke yakar kungiyoyin ‘yan ta’adda.
Wallafawa ranar:
Ministar tsaron Faransa Florence Parly ce ta bayyana shirin, tare da karin bayanin cewar, za a tura karin dakarun 600 zuwa yankin na Sahel ne nan da karshen watan Fabarairu da muka shiga.
Parley tace za a girke karin sojojin na Faransa a yankin da ya hada iyakokin Mali, Burkina Faso da kuma Nijar, domin murkushe barazanar hare-haren ta’addancin dake karuwa a yankin.
A wata sanarwar kuma rundunar sojin kasar ta Faransa tace za ta aika da karin dakarunta zuwa Sahel ne tare da motocin sulke kimanin 100.
A baya bayan nan dai kasashen Nijar, da Burkina Faso suka fi fuskantar hare-haren ta’addanci, inda a jamhuriyar ta Nijar kadai ‘yan ta’addan suka halaka sojoji sama da 150 a kasa da watanni 2, a hare-haren da suka kaiwa sansanonin sojin kasar a Inates da kuma Shinagodar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu