Isa ga babban shafi
Sudan

Kotun Sudan za ta rataye jami'an tsaron kasar 27 kan kisan farar hula

Wata kotu a Sudan ta zartas da hukuncin kisa kan wasu jami’an sirrinta 27 da aka samu da hannu wajen kisa da kuma azabtar da masu zanga-zangar adawa da gwamnati cikin shekarar nan.

Wasu jami'an tsaron Sudan yayin zanga-zangar kasar.
Wasu jami'an tsaron Sudan yayin zanga-zangar kasar. REUTERS/Thaier al-Sudani
Talla

Kotun karkashin mai shari’a Sadok Albdelrahman ya ce jami’an an same su da hannu dumu-dumu wajen azabtarwa baya ga kisan wasu fararen hula ciki har da kisan Ahmed al-Kheir malamin makaranta, wanda jami’an hukumar suka kama cikin watan Janairun da ya gabata suka kuma hallaka shi a shalkwatarsu.

Kotun dai ta bukaci aiwatar da kisa kan mutanen 27 ta hanyar rataya bayan hujjoji da suka nuna yanda suka zabtar da tarin jama’ar kasar ta Sudan lokacin zanga-zangar wadda ta faro daga watan Disamban bara.

Akalla dai mutane 177 aka tabbatar da mutuwarsu a hannun jami’an tsaron kasar ta Sudan yayinda wasu aka harbesu da harsashi a dandalin zanga-zangar bayan da shugaban kasar na wancan lokaci Omar Hasan al-Bashir ya baiwa jami’an tsaro cikakken ikon ladabtar da masu zanga-zangar.

Wasu majiyoyi na daban dai sun bayyana cewa adadin mutanen da suka mutu a zanga-zangar sun haura mutum 250.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.