Isa ga babban shafi

Fafaroma Francis ya bukaci wanzar da zaman Lafiya a duniya

Shugaban Darikar Katolika ta Duniya, Fafaroma Francis ya bukaci al’ummar duniya da ta samar da hasken da zai kawar da duhun da ke kunshe a zukatan bil’adama wanda shi ke ummul aba’isin zalunci da rashin adalci har ma da rikice-rikice da kuma matsalar kin-jinin bakin haure a cewarsa. 

Fafaroma Francis a garin hiroshima
Fafaroma Francis a garin hiroshima Vincenzo PINTO / AFP
Talla

A yayin jawabinsa na ranar Kirismai a fadar Vatican, Fafaroman mai shekaru 83 ya bukaci wanzar da zaman lafiya a kasashen Syria da Lebanon da Yemen da Iraqi da Veneuela da Ukraine da kuma wasu sassa na Afrika da ke fama da tashe-tashen hankula.

Kuna iya latsa alamar sauti da ke kasa domin sauraron abin da Limaman addinin na kirista a Najeriya da Nijar ke cewa dangane da wannan buki, cikin shiri na musamman kan bukukuwan kirsimeti tare da Ahmed Abba.

19:59

Shiri na musamman kan bukin kirsimeti 2019

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.