Isa ga babban shafi
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Ra'ayoyi kan tasirin dakarun kasashen ketare wajen yakar ta'addanci a Sahel

Wallafawa ranar:

Taron shugabannin kasashe 5 na yankin Sahel da ya gudana ranar lahadi a birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar, ya jaddada muhimmancin ci gaba da hulda da kasashen duniya don yaki da ta’addancin a yankin na Sahel.Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da, a wasu kasashe aka fara nuna shakku dangane da irin rawar da dakarun kasashen yammacin duniya ke takawa a wannan yaki.Menene ra’ayoyinku game da amfani ko rashin amfani dakarun kasashen ketare a wannan yaki?Anya yankin Sahel zai iya tabbatar da tsaron kansa ba tare da gudunmuwar kasashen ketare ba?Kan wannan batu muka baku damar tattaunawa da musayar ra’ayoyi.

Daya daga cikin dakarun Faransa dake yakar ta'addanci a Tin Hama, a kasar Mali.
Daya daga cikin dakarun Faransa dake yakar ta'addanci a Tin Hama, a kasar Mali. REUTERS/Benoit Tessier/File Photo
Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.