Burkina Faso
An kashe mutane a harin ta'addanci a Burkina Faso
‘Yan bindiga sun kashe mutane 15 lokacin da suke gudanar da ibada cikin wata mujami’a da ke garin Hantoukuoura jiya lahadi a gabashin gabashin kasar Burkina Faso.
Wallafawa ranar:
Talla
Bayanai sun ce ‘yan bindiga a kan babura sun kai hari kan wannan mujami’a ta mabiya darikar Protestant ne da ke lardin Foutouri kusa da iyakar kasar da Jamhuriyar Nijar kuma sanarwa da fadar gwamnan lardin Fadan Ngourma ta fitar ta ce mutane 14 ne suka rasa rayukansu a wannan hari.
Hare-haren ta'addaci ya tilastawa da dama daga mazauna yankunan arewacin kasar ficewa daga gidajen su.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu