Isa ga babban shafi
Burkina Faso

An kashe mutane a harin ta'addanci a Burkina Faso

‘Yan bindiga sun kashe mutane 15 lokacin da suke gudanar da ibada cikin wata mujami’a da ke garin Hantoukuoura jiya lahadi a gabashin gabashin kasar Burkina Faso.

Sojojin Burkina Faso a yankin Soum
Sojojin Burkina Faso a yankin Soum MICHELE CATTANI / AFP
Talla

Bayanai sun ce ‘yan bindiga a kan babura sun kai hari kan wannan mujami’a ta mabiya darikar Protestant ne da ke lardin Foutouri kusa da iyakar kasar da Jamhuriyar Nijar kuma sanarwa da fadar gwamnan lardin Fadan Ngourma ta fitar ta ce mutane 14 ne suka rasa rayukansu a wannan hari.

Hare-haren ta'addaci ya tilastawa da dama daga mazauna yankunan arewacin kasar ficewa daga gidajen su.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.