Isa ga babban shafi
Najeriya

Najeriya za ta fara ginin bututun gas daga kudu zuwa Arewa

Gwamnatin Najeriya na gab da fara aiki ginin bututun iskar gas da zai rika dakon gas daga kudanci zuwa arewaci a wani mataki na saukaka harkar safarar sinadarin baya ga fadada ayyukanta a sassan kasar.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari REUTERS/Carlo Allegri
Talla

Sanarwar da mai Magana da yawun shugaban Najeriyar Malama Garba Shehu ya fitar ta nuna cewa Nututun iskar gas din zai taso daga Ajaokuta zuwa Kaduna kana ya isa Kano don saukakawa al’umma.

Sanarwar ta Garba Shehu ta ruwaito shugaban Najeriyar Muhammadu Buhari yayin jawabinsa a taron kasashe masu fitar da iskar gas karo na 5 da ke gudana a Malabo na Equatorial Guinea na cewa suna kan hanyar fadada hanyoyin safarar iskar gas a cikin Najeriya gabanin dasa bututun da zai basu damar isar ga iskar ta gas ga sauran kasashen Nahiyar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.