Isa ga babban shafi
Afrika

Ana ci gaba da zanga-zanga a Algeria

Masu bore a Algeria sun gudanar da gaggarumar zanga-zanga a ranar juma’a a babban birnin kasar Aljas don nuna rashin amincewar su da ka’aidojin da hukumar zabe da gwamnatin rikon kwariya suka gindaya dangane da zaben Shugaban kasar da suka rage makwani biyu a yi.

Masu zanga-zangar adawa da zaben shugaban kasa a Algiers, babban birnin Algeria.
Masu zanga-zangar adawa da zaben shugaban kasa a Algiers, babban birnin Algeria. REUTERS/Ramzi Boudina
Talla

Tun bayan saukar Abdel Aziz Bouteflika tsohon Shugaban kasar,masu bore a kasar na zargin gwamnatin rikon kwariya da gudanar da salon siyasa mai kama da gwamnatin Abdel Aziz Bouteflika.

Masu zanga-zangar dauke da aluna sun bayyana cewa babu ta yada za aje wannan zabe mudin hukumomin dake nan ba su bi umurni jama’ar kasar ba.

Akalla mutane 25 ne yan Sanda suka kama biyo bayan wannan tarzoma ta jiya juma’a.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.