Afrika
Mutane 39 ne suka mutu a Kenya da Tanzania sanadiyar ruwan sama
Ruwan sama kamar da bakin kwarya mai dauke da iska yayi sanadiyar hallaka mutane 39 a kasashen Kenya da Tanzania.
Wallafawa ranar:
Talla
Rahotanni sun ce ruwan ya haifar da zabtarewar kasa da kuma rusa gidaje, abinda ya kai ga birne mutane 29 a Kenya, yayin da kogi kuma ya tafi da mutane 10 a Tanzania.
Ministan cikin gidan Kenya, Fred Matiang’i yace mutane 12 sun mutu ne a Tapach da Parua dake kudancin Pokot, yayin da 17 suka mutu a Tamkal dake tsaiyar Pokot.
Tuni aka tura sojoji da yan Sanda domin gudanar da aikin agaji.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu