Isa ga babban shafi
Wasanni-Kwallon kafa

Kwallon kafa: Najeriya ta sha kashi a wasan neman Olympics

Ivory coast ta doke Najeriya da ci daya mai ban haushi a gasar matasa ta ‘yan kasa da shekaru 23, inda ake fafutukar neman tikitin shiga gasar kwallon kafa ta Olamfik da zata gudana a birnin Tokyo na Japan, wasan farko na ruknuni na 2 da aka fafata a birnin Alkahira na kasar Masar.

Wasu daga cikin 'yan wasan tawagar Najeriya ta 'yan kasa da shekaru 23 a gasar Olamfik ta Rio 2016
Wasu daga cikin 'yan wasan tawagar Najeriya ta 'yan kasa da shekaru 23 a gasar Olamfik ta Rio 2016 GUSTAVO ANDRADE / AFP
Talla

Silas Gnaka ne ya saka kwallo a ragar Najeriya daga bugun – daga – kai – sai – mai- tsaron – raga, bayan wata rafka da dan wasan baya, Olisa Ndah ya yi, lamarin da ya kai ga ba shi jan kati saura minti 20 a tashi wasa.

Bayan wannan wasa ne fa aka barje gumi tsakanin Afrika ta kudu da Zambia, inda aka yi canjaras 0-0, ba kare – bin damo a filin wasa na Al Salam.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.