Sarakunan Afrika sun baiwa Paul Biya lambar yabo
Wata kungiyar sarakunan gargajiyar nahiyar Afrika da ta gudanar da wani taro a Jamhuriyar Benin,taron da ya samu halartar Shuwagabanin gargajiya da daga kasashen Afrika ya bukaci yan siyasar nahiyar su saka shuwagabanin gargajiya a cikin harakokin tafiyar da al’amuran mulki a nahiyar.
Wallafawa ranar:
Har ila yau taron ya karama Shugaban kasar Kamaru Paul Biya kan kokarin da yake wajen sake samar da zaman lafiya a kasar ta Kamaru.
Shugaban wannan kungiya da ake kira Panafrican Council of Traditional and Customary Authorities PACTCA, Dada Awiyan Octave Sarkin Dahe a jamhuriyar Benin ya bayyana Shugaban Kamaru Paul Biya a matsayin mutumen dake da hangen nesa.
Shugaban kungiyar ya na mai fatan Shugabanin Afrika za su yi koyi tareda saka Sarakunan gargajiya a lamuran yau da na kullum a hukumance.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu