Bakonmu a Yau
Farfesa Khalifa Dikwa kan sumamen jami'an tsaron Najeriya a cibiyoyin azabtar da yara
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:42
A Najeriya bisa dukkan alamu, Hukumomin kasar sun fara daukar matakan rufe cibiyoyin da ke azabtar da yara da matasa da sunan koya masu karatun addini. A dan tsakanin nan dai Jami'an tsaro sun rufe irin wadannan cibiyoyi a garuruwan Kaduna da Daura. Garba Aliyu Zaria ya tuntubi Farfesa Khalifa Dikwa mai sharhi game da lamurran duniya shin ko ya gamsu da daukan matakan da ake yi.