Yayi Boni ya nisanta kansa daga masu dasawa da Gwamnatin Benin
A Jamhuriyar Benin , jam’iyyar tsohon Shugaban kasar Yayi Boni ta nisanta kanta daga sanarwar da gwamnatin kasar ta fitar dake tabbatar da ita a matsayin jam’iyya mai cikkaken iko .
Wallafawa ranar:
Tsohon Shugaban kasar Boni Yayi a shafin sa na Facebook ya musanta sanarwar da gwamnatin shugaba Patrice Talon ta fitar ,ida ya bayyana cewa har kullum suna bangaren yan adawa, banda haka jam’iyyar su na nan daram dakam.
Daga cikin sanarwar da Gwamnatin kasar ta fitar dangane da ajam’iyyar tsohon Shugaban kasar ta FCBE,an canza wasu daga cikin membobinta,lamarin da ya haifar da ya’an jam’iyyar ta FCBE suka nisanta kan su da shi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu