Kotun Tunisia ta ki ba da belin Karoui don shiga zagayen zabe na 2
Kotu a Tunisia ta ki amincewa da bayar da belin Nabil Karoui, domin shirin zuwa zaben shugaban kasa zagaye na biyu, sakamakon nasarar da ya samu a zaben da aka yi a karshen mako.
Wallafawa ranar:
Talla
Lauyan Karoui, Kamal Ben Masoud yace zasu daukaka kara, bayan da alkalin kotun yace bashi da hurumin bada belin.
Ana tuhumar dan takarar ne da halarta kudaden haramun, kuma bisa dokokin kasar yana da hurumin tsaya takara har sai kotu ta same shi da aikata laifi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu