Isa ga babban shafi

Al'ummar Tunisia na dakon sakamakon zaben shugaban kasa

Dai dai lokacin da al'ummar kasar Tunisia ke dakon sakamakon zaben shugaban kasar da suka kada kuri'a a jiya Lahadi, biyu daga cikin 'yan takarar da da basu da alaka da gwamnati sun bayyana samun nasara, tun a sa'o'i kalilan bayan rufe rumfunan zaben irinsa na 2 a kasar tun bayan juyin juya halin 2011.

'Yan takarar neman kujerar shugabancin kasa a Tunisia
'Yan takarar neman kujerar shugabancin kasa a Tunisia Arab.com
Talla

Hukumar zabe a kasar ta Tunisia ta bayyana cewa kashi 45 na masu rijistar zabe ne suka kada kuri'unsu a zaben, matakin da ke nuna yadda aka samu raguwar masu kada kuriar kasa da kashi 64 da aka samu a 2014.

Kais Saied, masanin harkar shari'a da dokokin kasa da ya shiga zaben a matsayin dan takara mai zaman kansa, ya bayyana cewa shi ke kan gaba da yawan kuri'u, kamar yadda alkaluman farko suka nuna.

Magoya bayan Nabil Karaoui da ake tsare saboda zargin halarta kudaden haramun, na ta bayyana farin ciki a Ofishin yakin neman zabensa, bayan ya bayyana samun nasarar zuwa zagaye na biyu, duk da ya ke an gudanar da zaben ya na tsare.

Sauran fitattun 'yan takara sun hada da AbdelFatah Mourou da ke yiwa Jam'iyyar Ennahda takara, sai kuma Firaminista Youssef Chahed.

A gobe Talata ne ake sa ran bayyana cikakken sakamakon zaben.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.