Super Eagles ta kira Josh Maja na Bordeaux
Kungiyar Bordeuax ta tabbatar da kiran da Najeriya ta yi wa Josh Maja domin buga mata wasaan sada zumunta da Ukraine a ranar 10 ga watan nan na Satumba.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Maja dan shekaru 20, haifaffen Landan, amma dan asalin Najeriya, na da damar buga wa Super Eagles ko kuma tawagar Ingila kwallon kafa.
A watan jiya ne, kocin Super Eagles ya ce, ya gana da Maja a Faransa domin shawo kansa don amincewa ya buga wa kasarsa ta sali Najeriya tamaula.
Yan Najeriya da dama ne yanzu haka ke fatan ganin dan wasan yayi na’am da wannan tayi daga kungiyar kwallon kafar Najeriya .
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu