Isa ga babban shafi
Bakonmu a Yau

Farfesa Abdullahi Zuru kan hukuncin kotun Birtaniya da ya bai wa wani kamfani izinin kwace kadarorin Najeriya

Wallafawa ranar:

Wasu kungiyoyin fararen hula a Najeriya yau sun gudanar da zanga zanga a gaban ofishin Jakadancin Birtaniya da ke birnin Abuja, inda suke bukatar soke hukuncin kotun kasar da ya baiwa wani kamfani umurnin karbe kadarorin gwamnati da suka kai sama da Dala biliyan 9 da rabi, saboda sabawa wata yarjejeniyar kwangilar iskar gas.Kungiyoyin sun bayyana hukuncin kotun a matsayin haramcacce, inda suka bukaci gudanar da bincike kan wadanda ke da hannu wajen badakalar. Dangane da wannan zanga zangar da kuma hukuncin kotun da ya mallakawa kamfanin kadarorin Najeriya, mun tattauna da masanin harkar shari’a da kuma man fetur, Farfesa Shehu Abdullahi Zuru na Jami’ar Abuja, kuma ga tsokacin da yayi akai.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari Twitter/Asorock
Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.