Isa ga babban shafi
Bakonmu a Yau

Malam Muntari Hamisu mai rajin kare hakkin dan adama game da matakin hukuncin daurin rai da rai kan shugabannin 'yan aware a Kamaru

Wallafawa ranar:

Wata kotun Soja da ke birnin Younde a kasar Kamaru ta zartas da hukuncin dauri na rai da rai kan jagoran ‘Yan awaren yankin masu amfani da turancin Ingilishi Julius Sisiku Ayuk Tabe tare da wasu abokan gwagwarmayarsa 9. Tun jiya Talata da safe Kotun sojan ta zartas da hukuncin.Shi jagoran da wasu abokan nasa 46 sun nemi mafaka a Nigeria, amman kuma aka garkamesu a watan Janairu na bara kafin a tattarasu zuwa Younde, a kuma dankawa Hukuma. Mun nemi ji daga Malam Muntari Hamisu na kungiyoyin kare hakkin biladama a Kamaru wai shin ya ya ya ke kallon matakin hukuncin dauri na rai da rai kan ‘yan Awaren.

Jagoran 'yan awaren Kamaru Julius Sisiku Ayuk Tabe
Jagoran 'yan awaren Kamaru Julius Sisiku Ayuk Tabe YouTube
Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.