Isa ga babban shafi
Chad

Tubabben sarkin Abéché na kasar Chadi yaki fitcewa daga fada

Yanzu haka jami'an tsaro a kasar Chadi na kokwarin kwantar da hankula a wata masarautar Abeche dake Gabashin kasar a kokarin su na fitar da sarkin garin da iyalansa da mahukunta suka tube tare da maye gurbin sa da wani.Watanni da dama kenan bayan tsige shi daga karagar mulki, Sarkin kabilar Ouaddai da ke da babbar fadarsa a garin Abeche da ke Gabashin kasar Chadi ya ki fita daga wannan fada.Kuma duk da yunkurin yin amfani da jam'an tsaro da mahukunta suka yi domin fitar da shi, amma hakan ya gagara, sakamakon yadda dangi da kuma kabilar sarkin ke ci gaba da nuna tirjiya.watanni da sukagabata mahukuntan kasar suka sauke sarkin tare da maye gurbin sa da wani, sakamakon yawaitar tashin hankali da ake samu tsakanin kabilun makiyaya da Manomar yankin da ake ganin tsohon sarkin na da hannu a ciki, wajen baiwa kabilar sa ta Ouaddai fifiko.Dangane da wannan batu Sarkin Hausawan Ndjamena Alhaji Mustapha Ibrahim, ya yi mana karin bayani.

Masarautar Abeche dake Gabashin kasar Chadi.
Masarautar Abeche dake Gabashin kasar Chadi. AMAURY HAUCHARD / AFP
Talla

Latsa don sauraron karin bayani daga bakin sarkin hausawan Ndjamena Alhaji Mustapha Ibrahim.

03:06

Alhaji Mustapah Ibrahim, sarkin hausawan birnin Ndjamena, kan rikicin masarautar Ouaddai na Abeche a Gabashin kasar Chadi

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.