Isa ga babban shafi
DR Congo-Ebola

Congo na tuhumar jami'an lafiyarta 3 da kashe likitan WHO

Gwamnatin Jamhuriyar Dimokradiyar Congo ta tsare wasu ma’aikatan lafiya 3 bisa zargin su da kashe likitin Hukumar Lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya WHO da ke yaki da cutar Ebola a kasar.

Wasu jami'an lafiya da ke aikin yaki da cutar Ebola a Jamhuriyyar Demokradiyyar Congo
Wasu jami'an lafiya da ke aikin yaki da cutar Ebola a Jamhuriyyar Demokradiyyar Congo (WHO)
Talla

A ranar 19 ga watan Afrilun da ya gabata ne, aka harbe likitin na Hukumar Lafiyar dan asalin kasar Kamaru, wato Richard Valery Mouzoko Kiboung, a wani hari da aka kaddamar kan asibitin gabashin birnin Butembo.

Ma’aikatan Lafiyar kasar 3 da aka cafke saboda zargin su da hannu a kisan Likitan, za a tuhume su da aikata ta’addanci da kuma kitsa mummunan aiki kamar yadda mai shigar da kara na sojin kasar, Laftanar Kanar Jean Baptiste Kumbu Ngoma ya sanar.

An dai zargi mutanen 3 da gudanar da wani taron sirri a ranar 14 ga watan Afrilu, inda suka kitsa yadda za su salwantar da rayuwar likitan na Majalisar Dinkin Duniya.

Hukumar Lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce, ta tura jami’in na ta ne zuwa Jamhuriyar Congo domin shiga cikin tawagar da ke yaki da cutar Ebola wadda ta sake barkewa a cikin watan Agusta a arewacin Kivu.

Sai dai a bangare guda, Kungiyar Likitocin Cikin Gida ta bayyana bacin ranta kan cafke ‘ya’yanta, ta na mai cewa, za ta tsunduma cikin yajin aiki muddin aka gaza sako su cikin sa’o’i 48.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.