Isa ga babban shafi

Mulkin Najeriya da wahala - IBB

Tsohon shugaban mulkin sojin Najeriya, Janar Ibrahim Badamasi Babangida ya ce mulkin Najeriya akwai wahala.

Ibrahim Babangida tsohon shugaban Nigeria
Ibrahim Babangida tsohon shugaban Nigeria REUTERS/Luc Gnago
Talla

Ya bayyana Najeriya a matsayin kasa mai sarkakiya da wahalar tafiyarwa saboda yanayin al’ummar ta da bambance – bambancensu.

A cewarsa, bambance – bambancen sun kawo ra’ayoyi mabambamta tare da muhawwara zafafa,wadda wani lokaci ke kaiwa ga kiyayya da tashin hankali.

Da yake jawabi a Minna ta jihar Neja a Najeriya, yayin ziyarar da wasu shugabannin marasa rinjaye na majalisar wakilan kasar karkashin jagorancin Ndudi Elumelu suka kai mai a gidansa, Babangida ya bayyana Najeriya a matsayin kasa mai karsashi da ban sha’awa.

Ya bukaci ‘yan siyasa da kada su karaya da sarkakiyar kasar, maimakon haka su mayar da hankali wajen ciyar da ita gaba ta wajen amfani da yanayin al’ummarta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.