Isa ga babban shafi
Habasha

Tarzomar masu 'yan aware ta kai ga kisan mutum 4 a Habasha

Akalla Mutane 4 suka mutu sakamakon harbin bindiga a kudancin a Birnin Hawassa da ke kasar Habasha inda aka samu arangama tsakanin masu goyan bayan ballewar Yankin da jami’an tsaro.

Firaministan Habasha Abiy Ahmed
Firaministan Habasha Abiy Ahmed AFP/Monirul BHUIYAN
Talla

Kafofin yada labaran kasar sun ce jami’an tsaro sun kama mutane da dama yayin gudanar da zanga zangar 'yan awaren a yankin kudancin kasar.

Kabilar Sidama, wadda ita ce tafi yawan jama’a a kudancin Habasha na bukatar yancin cin gashin kai, daya daga cikin matsalolin siyasar da yanzu haka suka mamaye gwamnatin Firaminista Abiy Ahmed.

Ko a watan jiya, sai da kasar ta Habasha ta fuskanci yunkurin juyin mulki da ya kai ga tashin hankali a kasar, wadda ke farfadowa daga rikicin kabilanci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.