Tarzomar masu 'yan aware ta kai ga kisan mutum 4 a Habasha
Akalla Mutane 4 suka mutu sakamakon harbin bindiga a kudancin a Birnin Hawassa da ke kasar Habasha inda aka samu arangama tsakanin masu goyan bayan ballewar Yankin da jami’an tsaro.
Wallafawa ranar:
Kafofin yada labaran kasar sun ce jami’an tsaro sun kama mutane da dama yayin gudanar da zanga zangar 'yan awaren a yankin kudancin kasar.
Kabilar Sidama, wadda ita ce tafi yawan jama’a a kudancin Habasha na bukatar yancin cin gashin kai, daya daga cikin matsalolin siyasar da yanzu haka suka mamaye gwamnatin Firaminista Abiy Ahmed.
Ko a watan jiya, sai da kasar ta Habasha ta fuskanci yunkurin juyin mulki da ya kai ga tashin hankali a kasar, wadda ke farfadowa daga rikicin kabilanci.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu