Isa ga babban shafi
Wasanni

Za a tantance zakarar kwallon Afrika ta bana tsakanin Algeria da Senegal

Algeria da Senegal sun samu nasarar kaiwa matakin wasan karshe na gasar cin kofin nahiyar Afrika, bayan doke Najeriya da Tunisia a fafatwar da suka yi jiya.

Dan wasan Algeria Riyad Mahrez (daga dama) yayin murnar kwallon daya jefa a ragar Najeriya.
Dan wasan Algeria Riyad Mahrez (daga dama) yayin murnar kwallon daya jefa a ragar Najeriya. AFP
Talla

Algeria tasamu nasararta ce da 2-1, ta hannun dan wasan Najeriya Troost-Ekong da ya jefa kwallo a ragarsu bisa kuskure, sai kuma dan wasan kasar ta Algeria Riyad Maharez da ya jefa kwallo ta biyu a mintunan karshe bayan samun damar bugun tazara.

A bangaren Najeriya kuwa Odion Ighalo ne ya jefa mata kwallo a ragar Algeria.

Ita kuwa Senegal ta yi nasarar doke kasar Tunisia ce da 1-0.

Da fari kasashen sun fafata wasan tsawon mintuna 90 ba tare da samun nasarar jefa kwallo a ragar juna ba, duk da cewa kowannensu ya samu damar bugun daga kai sai mai tsaron raga.

A karin lokacin mintuna 30 ne Senegal ta samu nasara, bayanda dan wasan Tunisia Dylan Bronn yayi kuskuren jefa kwallon a ragarsu.

A yanzu za a fafata wasan neman na uku ranar laraba 17 ga watan Yuli, tsakanin Najeriya da Tunisia, sai kuma tantance kasar daza ta zama zakarar bana a gasar cin kofin Afrika tsakanin Algeria da Senegal a ranar Juma’a 19 ga watan na Yuli.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.