Mutane da dama ne suka mutu a harin Al Shebab a Kismayo
Majiyar tsaron kasar Somalia ta sanar da kawo karshen samamen da wasu yan kungiyar Al Shebab suka kai wani Otel tareda yi garkuwa da mutane a wannan wuri dake Kismayo.
Wallafawa ranar:
Yan Al Shebab dauke da manyan makamai sun yi garkuwa da wasu mutane a wani gidan Otel dake Kismayo.
Jami’an tsaro sun share daren jiya suna kokarin kubutar da mutanen dake cikin wanan Otel.
Majiyar tsaro Somalia ta bayyana mutuwar mutane 12 daga cikin mutanen da suka rasa ran su akwai wani Minista da wani dan Majalisa, yayinda wasu 30 suka samu raunuka.
Jami’an tsaro na ci gaba da gudanar da bincike domin tanttance masu bayar da goyan baya zuwa yan kungiyar Al Shebab a wadanan hare-hare dake hadasa mutuwar jama’a da dama a kasar ta Somalia.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu