Dr Dauda Muhammed Kontagora kan rahoton Oxfam da ya nuna tsananin rashin daidaito a kasashen yammacin Afrika
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:32
Kungiyar OXFAM ta yi zargin cewar ana cigaba da samun wagegen gibi tsakanin masu hali da marasa shi a Yankin Afirka ta Yamma, inda attajirai ke kara azircewa, yayin da talakawa ke kara talaucewa.
Rahotan yace yayin da wasu kasashe irin su Cape Verde da Mauritania da Senegal ke daukar matakan gyara domin fitar da mutane daga talauci, matsalar sai kamari take a kasashe irin su Najeriya da Nijar da kuma Saliyo.
Dangane da wannan rahoto mai tada hankali, mun tatauna da masanin tattalin arziki, Dr Dauda Muhammed Kontagora, kuma ga abinda yake fadi dangane da rahotan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu