Isa ga babban shafi
Mali-Sahel

MDD na nazarin sanya takunkumai kan 'yan kasar Mali

Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya ya fara nazari game da bukatar da Faransa ta gabatar, domin sanya takunkumai a kan wasu mutane biyar da ke haddasa tarnaki wajen samar da zaman lafiya a Mali, cikinsu har da wani dan majalisar dokoki daga jam’iyya mai mulkin kasar.

Sojojin Majalisar Dinkin Duniya na Minusma a Konna dake yankin Mopti na kasar Mali
Sojojin Majalisar Dinkin Duniya na Minusma a Konna dake yankin Mopti na kasar Mali MINUSMA/Gema Cortes
Talla

A ranar Alhamis ne Faransa ta gabatar da wannan bukatar a gaban Kwamitin Sulhun na Majalisar Dinkin Duniya, dauke da jerin sunayen mutanen biyar, da take neman a sanya masu takunkumai da kuma kwace masu kaddarori saboda suna hana samun zaman lafiya a kasar ta Mali.

Daga cikin mutanen biyar akwai Houka Houka Ag Alhousseini wanda jagoran masu da’awar jihadi ne a Tumbuktu, sai kuma Mahri Sidi Amar Ben Daha wanda ya assasa ayyukan jihadi a garin Gao duk a Arewacin kasar.

Sauran sun hada da Mohamed Ould Mataly wanda dan majalisar dokoki ne daga jam’iyyar mai mulki, sai kuma Mohamed Ben Ahmed Mahri dan kasuwa da ya yi kaurin suna wajen fataucin miyagun kwayoyi tsakanin kasashen Mali, Niger, Mauritania da kuma Burkina Faso.

Na biyar shi ne Ahmed Ag Albachar da ke jagorantar wata kungiyar ayyukan jinkai a Kidal. Mambobi a Kwamitin Tsaron na da damar daukar mataki game da wannan bukata ta Faransa kafin ranar talatar makon gobe.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.