Isa ga babban shafi
Najeriya-Zamfara

'Yan bindiga sun hallaka mutane 47 a kauyukan Zamfara 2

A Najeriya, akalla mutane 47 wasu ‘yan bindiga suka hallaka a wani farmaki da suka kai kauyukan Mallamawa da Tungar Kafau da ke karamar hukumar Shinkafi ta jihar Zamfara cikin tsakaddaren jiya Juma’a.

Wasu da suka gujewa kauyukansu saboda tsoron hare-haren 'yan bindiga
Wasu da suka gujewa kauyukansu saboda tsoron hare-haren 'yan bindiga rfihausa
Talla

Yayin zantawa da sashen hausa na RFI, wani mazaunin garin ya shaida mana cewa ‘yan bindigar sun hallaka mutane 40 a garin Mallamawa yayinda suka hallaka wasu Karin 7 a tungar Kafau.

A cewar shaidan wanda ya nemi a sakaya sunansa, kawo yanzu fargaba ta hana sallatar mutanen da ‘yan bindigar suka kashe saboda tsoron kar su juyo da wani sabon farmaki.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.