Kamaru
Mayakan Boko Haram sun hallaka mutane 26 a arewacin Kamaru
Jami’an tsaro a kasar Kamaru sun sanar da cewa mayakan kungiyar BokoHaram sun kashe mutane 26 a harin da suka kai Yankin Arewacin kasar a daren ranar lahadi.
Wallafawa ranar:
Talla
Wata majiyar soji tace sojoji 17 da fararen hula 9 aka kashe sakamakon fafatawar da jami’an tsaro suka yi da mayakan a Darak, wani tsibiri dake kusa da tafkin Chadi.
Majiyar sojin tace an kama mayakan 40, yayin da sojoji 7 suka bata.
Wannan shi ne hari mafi muni da mayakan suka kai a cikin ‘yan watanni da suka gabata.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu