Isa ga babban shafi
Sudan

Sudan za ta tsunduma yajin aikin gama-gari saboda mulki

Jagororin masu zanga-zanga a Sudan sun bukaci gudanar da yajin aikin gama-gari na tsawon kwanaki biyu wadda za a fara a ranar Talata mai zuwa biyo bayan gaza cimma matsaya tsakaninsu da sojojin kasar dangane da kafa mulkin farar hula a kasar.

Masu zanga-zanga a Sudan sun kifar da gwamnatin Omar al-Bashir
Masu zanga-zanga a Sudan sun kifar da gwamnatin Omar al-Bashir 路透社
Talla

An jingine tattaunawa tsakanin bangarorin biyu tun a ranar Litinin da ta gabata sakamakon yadda suka samu banbancin ra’ayi kan wanda zai jagoranci sabuwar gwamnatin kasar.

Jagororin zanga-zangar sun ce, a yanzu babu wani zabi da ya wuce tsunduma cikin yajin aikin gama-gari kamar yadda sanarwar da suka fitar ke cewa.

Yajin aikin dai zai shafi cibiyoyin gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu a cewar masu zanga-zangar da suka yi nasarar ganin bayan mulkin Omar al-Bashir.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.